1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kashe wani sojin Majalisar Ɗinkin Duniya a Mali

August 16, 2014

Majiyar tsaro a Mali ta ce wani sojin rundunar wanzar da zaman lafiya ta MDD ɗan asilin ƙasar Burkina Faso ya mutu, a harin ƙunar baƙin wake, kana wasu biyar suka jikkata.

https://p.dw.com/p/1Cvri
MINUSMA Soldaten UN Mission Mali
Hoto: AFP/Getty Images

Masu yin jahadin sun kai harin ne da wata motar da ke maƙare da abubuwan da ke fashewa a harabar rundunar ta wanzar da zaman lafiya ta MINUSMA da ke a garin Ber wanda ke da nisan kilomita 60 daga birnin Timbuktu.

Yawancin dakarun da ke cikin wannan runduna dai 'yan ƙasar Burkina Faso ne. Mayaƙan masu kaifin kishin addini waɗanda suka mamaye arewacin Mali tun a shekarun 2012 kafin daga bisanin dakarun ƙasashen duniya su koresu,sun daɗa kai hare-hare a Mali a 'yan kwanakin baya-baya nan.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Zainab Mohammed Abubakar