1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kara wa'adin dakarun kiyaye zaman lafiya a Mali

Suleiman Babayo
June 28, 2019

Yayin wani zama Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da kara wa'adin dakarun kiyaye zaman lafiya a Mali na tsawon shekara guda zuwa karshen watan Yuni na 2020.

https://p.dw.com/p/3LIy0
Deutschland Militär l Bundeswehr in Mali
Hoto: picture alliance/dpa/M. Kappeler


Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da kara tsawon waA'din dakarun kiyaye zaman lafiya na majalisar da ke kasar Mali. Kwamitin ya ce yanayin da ake cikin a watanni shida da suka gabata na tashe-tashen hankula suka janyo amincewa da kara zaman sojojin kasashen duniya har zuwa karshen watan Yuni na shekara mai zuwa ta 2020, inda aka kara wa'adin da tsawon shekara guda.

Gaba daya mambobin Kwamitin Sulhun na Majalisar Dinkin Duniya suka amince da wannan mataki. Francois Delattre ke zama jakadan Faransa a Majalisar Dinkin Duniya wanda ya nuna gamsuwa da wannan mataki.