1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kammala zaɓuka a ƙasar Kamarun

Usman ShehuSeptember 30, 2013

'Yan ƙasar Kamarun sama da miliyan biyar da aka yi wa rijistar zaɓe, suka isa rufuna don zaɓar wakilai a majalisar dokoki da ƙananan hukumomi

https://p.dw.com/p/19rwo
Cameroon president Paul Biya speaks to journalists following a meeting with French president at the Elysee Palace on January 30, 2013 in Paris. Biya is in Paris on a working visit to meet French business leaders. AFP PHOTO / PATRICK KOVARIK (Photo credit should read PATRICK KOVARIK/AFP/Getty Images)
Paul Biya shugaban kasar KamarunHoto: Patrick Kovarik/AFP/Getty Images

A ƙasar Kamarun ranar Litinin ɗinnan aka gudanar da zaɓen 'yan majalisar dokoki da na ƙananan hukumomi, inda ake ganin jam'iyyar CPDM ko kuma RDPC da ke mulkin ƙasar tun samun yancin kai, babu ɗaya biyu sai ta karkata sakamakon don ta yi nasara. Shugaba Paul Biya ɗan shekaru 80 da haifuwa tun sama da shekaru 30 ya ke kan mulki, a bariya ya sake lashe zaɓe shugabancin kasar, kuma sau uku yana ɗage zaɓen 'yan majalisar dokokin, a wani abin da yan adawa suka ce duk hanya ce ta yadda zai tabbatar ya birkita al'amura, domin jam'iyyarsa ta ci gaba da kasancewa da rinjaye a majalisar dokoki. Babbar jam'iyyar adawa ta Social Demokrat wato SDF, ita ce ke bi a baya, kana akwai wasu ƙananan jam'iyyu 41 da ke fafatawa kan kujeru 180.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Mouhamadou Awal