1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kammala shirye-shiryen zaben kasar Mali

July 27, 2013

A ranar Lahadi ake sa ran miliyoyyin 'yan kasar Mali za su zabi sabon shugaban kasa.

https://p.dw.com/p/19FHA
Hoto: Katrin Gänsler

A ranar Lahadi miliyoyin 'yan kasar Mali za su gudanar da zaben shugaban kasa-abin da ake sa ran zai kawo karshen rikicin siyasa na watanni 18 da ya kai fafatawa da kungiyoyi masu dauke da makamai.

'Yan takara 27 da ke neman kujerar shugabancin kasar sun kwashe makonni uku suna yakin neman zabe cikin lungu da sakon kasar. A ranar Jumma'a aka kawo karshen yakin neman zabe, kuma babu wani tashin hankalin da aka samu.

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Ban ki-moon da shugaban gwamnatin rikon kwaryar kasar ta Mali,Dioncounda Traore, duk sun amince da kalubalen da kasar ke fuskanta, sannan suka nemi 'yan kasar ta Mali su mutunta sakamakon zaben.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Halima Balaraba Abbas