1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Habasha ta kama 'yan adawa

Abdoulaye Mamane Amadou MNA
July 6, 2020

Hukumomi a Ethiopiya wato Habasha sun kama wasu kusoshin jam'iyyar adawa biyar bisa zarginsu da hannu a rikicin da ya barke sakamakon mutuwar shahararren mawakin nan dan kabilar Oromo a makon da ya gabata.

https://p.dw.com/p/3erR9
USA Protest gegen Ermordung eines äthiopischen Sängers
Hoto: picture-alliance/AP/E. Frost

Shugaban jam'iyyar nan mai fafatukar samun 'yancin Oromo ta (OLF) Dawud Ibsa ya bayyana cewa duk da kama kusoshin jam'iyyar har kawo yanzu ba a bayyana wasu muhimman dalilan da suka sa aka kama membobin jam'iyyar ba.

A makon da ya gabata ne rikici ya barke a babban birnin kasar ta Habasha wato Addis Ababa da yankin Oromiya, sakamakon mutuwar mawaki Hachalu Hundessa dan kabilar Oromo, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 156 ciki har da jami'an 'yan sanda 11, baya ga wasu akalla 170 da suka jikkata a yayin tashin hankalin, wanda ke zaman mafi tsanani tun bayan darewar firaminsitan kasar Abiy Ahmed kan madafun iko.