An kai harin a wani otel a Mali
August 7, 2015Talla
Shi dai otel din na Byblos shi ne wanda akasarin ma'aikatan samar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya a kasar ta Mali ke halarta, inda kawo yanzu aka samu rasuwar mutum daya a cewar wata majiyar tsaron kasar. Mutanen da ba a tantance ba sun kai harin ne a wannan otel da ke bisa hanya mai zuwa filin jirgin saman birnin na Sevare, inda kawo yanzu dakarun kasar ta Mali suka yi wa wajen tsinke a kokarin da suke na dakile wannan hari.
Wasu shaidun gani da ido na ganin cewa harin wani yunkurin sace mutane ne.