1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An gargadi al'ummar Masar da su guji tada rikici

July 22, 2013

Majalisar ministocin Masar ta yi kira ga jama'ar kasar da jam'iyyun siyasa da su tabbata sun guji tashin hankali yayin gangami ko zanga-zangar da su ke gudanarwa.

https://p.dw.com/p/19BZp
Egyptian supporters of the Muslim Brotherhood and deposed president Mohamed Morsi deploy a giant national flag during a rally outside Cairo's Rabaa al-Adawiya mosque on July 12, 2013, following Friday noon prayer. Activists for and against ousted Morsi have called rival rallies for the first Friday of Ramadan, as tensions soar over the army's overthrow of the Islamist leader. AFP PHOTO/MARWAN NAAMANI (Photo credit should read MARWAN NAAMANI/AFP/Getty Images)
Hoto: Marwan Naamani/AFP/Getty Images)

Majalisar ministocin ta yi wannan gargadi ne yayin taronta na farko da ta gudanar a wannan Lahadi (21.07.13) inda ta yi kira ga al'ummar kasar da su bada gudumawarsu ga sabon kwamitin da aka girka a kasar wanda zai yi garambawul ga kundin tsarin mulkin Masar din gabannin zaben 'yan majalisun dokokin kasar.

A daura da wannan, wani tashin hankali da aka samu a kasar ta Masar ya yi sanadiyyar kisan wasu sojoji biyu da dan sanda guda a yankin nan na Sinai yayin da daruruwan mata suka yi wani maci zuwa ma'aikatar tsaron kasar domin nuna fushinsu sakamakon kisan wasu mata uku da aka yi a wani gangami da magoya bayan hambararren shugaban Masar din Muhammad Mursi su ka yi a Mansura a ranar Juma'ar da ta gabata.

Zanga-zanga a Masar dai a dan tsakanin nan ta zama tamkar jamfa a Jos tun bayan da sojin kasar su ka hambarar da gwamnatin Mursi daga gadon mulki a farkon wannan watan.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Saleh Umar Saleh