1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An cimma sulhu a Jamhuriyar Demokaradiyyar Kwango

December 31, 2016

'Yan adawa da gwamnati a Jamhuriyar Demokaradiyyar Kwango sun cimma sulhu bayan da aka kwashe makonni biyu ana tataunawa da nufin warare rikicin siyasar kasar.

https://p.dw.com/p/2V54I
Demokratische Republik Kongo Joseph Kabila in Bata
Hoto: Getty Images/AFP/C. De Souza

 

Rikicin siyasar dai ya  samo asili ne bayan da shugaba Joseph Kabila ya ki sauka daga mulki a karshen wa'adinsa a ranar 20 ga wannan wata na Disamba da ke shirin kammala.Wani kakakin jami'an Cocin Roman Katolika na kasar da ke shiga tsakanin ya ce yau aka shirya za a baiyana sanarwa yarjejeniyar da za a  rataba hannu a kanta.Kuma daya daga cikin abubuwan da yarjejeniyar ta tanada shi ne cewar joseph kabila zai ci gaba da yin mulki har zuwa sabuwar shekara ta 2017,lokacin da a aka shirya yin wani sabon zabe a kasar, sannan za a nada sabon firaminista da ya fito daga bangaran 'yan adawa.