1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An baiyana sakamakon zaben'yan majalisu a Cote d'Ivoire

December 21, 2016

Hadin gwiwar jam'iyyun siyasar da ke yin mulki sun sami rinjaye a zaben 'yan majalisun dokokin da aka gudanar.

https://p.dw.com/p/2UdQq
Elfenbeinküste Referendum Wahl Abidjan
Hoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

Kawancen jam'iyyun masu goyon bayan shugaba Alassane Ouattara sun sami kujeru 167 a cikin 254.Wannan shi ne zabe na farko da aka gudanar a kasar a karkashin sabon kudin tsarin mulki na kasar wanda shugaba Outtara ya kaddamar da kwaskwarima a kansa.'Yan adawar wadanda suka kauracewa zaben a shekara ta 2011 a yanzu zasu sake dawowa a  majalisar dokokin ta Cote d'Ivoire.