An sallamo tsohon Firaministan kasar Malesiya
September 20, 2018Talla
An sallamo tsohon Firamistan kasar Malesiya Najib Razak bayan da hukumar yaki da yiwa dukiyar kasar ta'annati tsare a ranar Laraba sakamakon wasu kudade da aka same shi da su ajiye a banki.
Tun da fari an zargi tsohon Firaministan da laifin cin hanci da rashawa kafin daga baya a kuma bankado wasu laifuffuka har 25 da suka hada da amfani da mukamin sa wajen cin amanar kasar, kodayake ya karyata wadannan zarge-zarge.
Babbar kotun kasar dai ta bayar da belinsa kan kudi Dala dubu dari 845.