'Yan majalisar daijai na Amirka sun takawa Trump birki
March 14, 2019Talla
Wakilai majalisar 54 suka kada kuri'a a kan kudirin yayin da 46 suka hau kujerar naki bakwai daga cikinsu kuwa 'yan jam'iyyar ta Republican. Masu aiko da rahotanni sun ce kisan dan jaridar nan na Saudiya Jamal Khasshogi da aka yi a cikin watan Oktobar shekara bara na daga cikin dalilan da suka sa 'yan majalisar datijan, suka takawa shugaba Trump birki a game da batun tallafin makamai da Amirka ke bai wa Saudiya a yakin da take yi da Yemen.