Amirka za ta bai wa Afirka Tallafi
August 6, 2014Talla
Obama ya ce za su saka hannun jari na tsawon lokaci da sannu a hankali a nahiyar ta Afirka ya ce ba za su iya kauda kai ba, ga sabuwar nahiyar da ke samun ci-gaba ta fannin tattalin arziki.
Haka shugaban na Amirka ya sanar da samar da biliyan 26 a wani shiri na samar da wutar lantarki a cikin ƙasashen yankin kudu da hamada. Barack Obama ya bayyana haka ne a taron Amirka da ƙasashen Afirka da ake daf da kamalawa a yau, wanda ya samu hallartar shugabannin ƙasashen Afirka kusa guda 40.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu