1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka tace jiragen UAE sun kai farmaki a Libya

August 26, 2014

Bayanan sirri da mahukuntan daular larabawa ba su tabbatar da sahihancinsu ba sunce jiragen nan da suka kaddamar da hare-hare a Libya a kwai na UAE a ciki.

https://p.dw.com/p/1D1Mm
Libyen Luftangriff auf Tripolis
Hoto: Reuters

Wasu jiragen yaki mallakar daular larabawa ta UAE sun yi ruwan bama-bamai cikin sirri kan mayakan sakai a Libya, adaidai lokacin da rikicin wannan kasa ke kara tsamari bayan da mayakan sakan Islama suka bayyana sunan Firemiyansu daga bangaren na 'yan tawaye da ke adawa.

Jamian Amirka sun tabbatar da cewa, a ranar Litinin jiragen yakin na daular larabawa ta UAE sun kai wasu hare-hare har sau biyu cikin kwanaki 7 ta hanyar amfani da wasu sansanoni a Masar.

Wani jami'i daga daular larabawan ya fada wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa babu wani abu da mahukuntan kasar sa suka fitar a dangane da rahotannin da ke fita a dangane da wannan farmaki. Shima wani jami'in Amirka da bai so a bayyana sunansa ba yace rahotannin haka suke.

Mawallafi: Yusuf Bala
Edita: Umaru Aliyu