Amirka ta shawarci kungiyar kasashen nahiyar a kan Venezuela
June 4, 2018Talla
Sakataren harkokin wajen Amirka Mike Pompeo ya kuma yi Allah wadai da zaben da aka gudanar a watan da ya gabata a kasar ta Venezuela, wanda ya sake bai wa shugaban kasar Nicolas Maduro damar cigaba da shugabancin kasar.
Da yake mayar da martani ministan harkokin kasashen wajen Venezuela ya zargi kasar Amirka da karya sharuddan zaman taren da kungiyar ta yi tanadi sakamakon takunkumin da ta kakaba wa Venezuelan tun a baya.