1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Amirka ta jajanta rikicin yankin Tigray

March 18, 2021

Ana sa ran cewa shugaban kasar Amirka Joe Biden zai tura da wakili zuwa kasar Habasha don nuna alhininsa kan yakin da ya auku a yankin Tigray na kasar ta Habasha.

https://p.dw.com/p/3qpq7
USA Washington | Joe Biden zum Coronahilfspaket
Hoto: Patrick Semansky/AP Photo/picture alliance

Shugaba Biden zai tura da Sanata Chris Coons da ke zama na hannun damansa kasar, kana kuma ya tuntubi kungiyar Tarayyar Afirka. Ana kuma sa ran Coons zai bar Amirka zuwa Habasha a wannan rana ta Alhamis.

Duk da yake gwamnati ta ce an daina yaki a yanki amma ta yi amannar cewa ana kai hare-hare ta bayan fage. Dubban mutane ne dai suka rasa rayukansu yayin da dubban daruruwa suka rasa matsugunansu wasu kuma ke bukatar abinci da ruwa da kuma magunguna a yankin da ke da yawan al'umma kimanin miliyan biyar.