1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jigo a gwamnatin Amirka zai kai ziyara Afirka

November 12, 2021

A mako na gaba ne Sakataren harkokin wajen Amirka Antony Blinken zai fara ziyarar aiki a kasashen Kenya da Najeriya da kuma Senegal da ke nahiyar Afirka.

https://p.dw.com/p/42ug6
Strategischer Dialog zwischen USA und Ukraine
Hoto: Leah Millis/AP/Reuters/dpa/picture alliance

A birnin Nairobi na kasar Kenya, Blinken zai gana da shugaba Uhuru Kenyatta don tattauna matakin kawo karshen annobar coronavirus da kuma batun tsaro a kasashen Habasha da Somaliya da kuma Sudan, kasancewar Kenyar na zama mamba a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya.

A cikin makon Blinken zai isa Najeriya don tattaunawa da shugaba Muhammadu Buhari kan hadin gwiwa a fanonnin tsaro da fadada samun makamashi da farfado da dimokradiyya. Yayin da a Dakar, sakataren zai gana da shugaba Macky Sall na Senegal kan jaddada hadin gwiwar kasashen biyu.