1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaba Ouattara ya kafa jam'iyyar RHDP a Cote d'Ivoire

Gazali Abdou Tasawa
July 17, 2018

A kasar Cote d'Ivoire Shugaba Ouattara ya kaddamar a jiya Litinin da sabuwar jam'iyyarsa ta RHDP a wani mataki na tunkarar zabukan da ke tafe a kasar da suka hada da na shugaban kasa. 

https://p.dw.com/p/31Zah
Elfenbeinküste - Präsident Ouattara
Hoto: picture alliance/AA/M. Wondimu Hailu

Jam'iyyar RDR ta Shugaba Alassane Ouattara da jam'iyyar UDPCI ta Albert Toikeuse Mabri mai kujeru shida a majalisa da kuma wasu manyan 'yan siyasar kasar masu da'awar bin akidar tsohon shugaba marigayi Houhouete Boigny ne suka hade wuri daya domin kafa wannan sabuwar jam'iyya ta RHDP. 

Bayan muhawara ta sama da awa daya da babban taron jam'iyyar ya gudana a birnin Abidja ya zabi Shugaba Ouattara a matsayin shugaban sabuwar jam'iyyar. Tun farko dai jam'iyyar PDCI ta Henry Konan Bedie babbar abokiyar kawancen mulki da jam'iyyar RDR ta Shugaba Ouattara ta ki amincewa da shirin shugaban na hade jam'iyyunsu wuri daya domin kafa wannan sabuwar jam'iyya.