1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

AFCON: Koulibaly ya mayar wa da Napoli martani mai zafi

August 4, 2022

Dan wasan Senegal Kalidou Koulibaly da ya fice daga Napoli a cikin shekarar nan, ya soki matsayar mamallakin Napolin da ke son hana 'yan wasansa da ke da tushe da Afirka zuwa gasar AFCON.

https://p.dw.com/p/4F63N
Udinese Calcio vs Chelsea FC | Kalidou Koulibaly
Hoto: Ettore Griffoni/NurPhoto/picture alliance


Dan wasan baya a kungiyar kwallon kafa ta Chelsea Kalidou Koulibaly, ya yi kira ga mamallakin tsohon kulob dinsa na Napoli ta lig din Serie A na Italiya da ya mutunta kungiyoyin kwallon kafa na Afirka, a daidai lokacin da furucin jami'in na Napoli ke ci gaba da fusata 'yan kwallon kafar Afirka da ke Turai.


A ranar Talata ce dai aka ruwaito  Aurelio De Laurentiis na cewa daga yanzu ba zai sanya hannu a kwantaragi da wani dan kwallo na Afirka ba, har sai dan wasan ya amince a rubuce cewa ba zai shiga gasar kwallon kafar Afirka ta AFCON ba. Mai kulob din Napolin, ya ce ya lura a duk lokacin da aka zo gasar AFCON ba ya samun hankalin 'yan wasansa na Afirka.