1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Adama Barrow zababben al'ummar Gambiya a 2016

Yusuf Bala Nayaya
January 9, 2017

Zaben watan Disambar bara ya zama zakaran gwaji na gwada karfin ‘yan adawa a kasar, ya kuma zama zaben da sakamakonsa ya ba wa Shugaba Yahya Jammeh shan kayi.

https://p.dw.com/p/2VLJ8
Gambia Präsidentschaftswahl Adama Barrow
Hoto: Getty Images/AFP/STR

Farkon rayuwa da karatu

Shi dai Barrow an haife shi a ranar 16 ga watan Fabrairu na 1965 a Mankaman Kunda, wani karamin kauye na Jimara kusa da garin Basse mai makwabtaka da kogin Gambiya, ya yi makarantar firamare ta Koba Kunda da sakadaren Crab Island a birnin Banjul kafin daga bisani ya samu tallafin karo karatu ya je makarantar  Muslim High School,  bayan kammala wannan makaranta ya yi aiki da wani kamfani mai zaman kansa kafin daga bisani ya tafi birnin London na Birtaniya, ya yi karantu a fannin  da ya shafi harkar gidaje da filaye a farkon shekarun 2000 a lokacin da ya ke karatu ya na kuma aiki da wani babban kantin siyar da kayayyaki na Argos a matsayin jami'in tsaro dan samun kudade ya  dauki  nauyin karatun da ya ke yi.

Barrow  ya koma gida Gambiya  bayan kammala karatunsa, a shekarar 2016 inda ya kafa kamfanin hada-hadar gidaje da filaye na Majum Real Estate ya zama baban shugaban kamfanin.

Idan muka koma bangaren siyasa a shekarar 2016 kawancen jam'iyyun siyasa suka zabi Barrow dan ya yi musu takara ta shugabancin kasar ta Gambiya , Kafin dai wannan lokaci bai taba rike wani babban mukami na siyasa ba, baya ga rike ma'ajin jam'iyyar UDP daya cikin jam'iyyun adawa a Gambiya.

Gambia Wahlen Yahya Jammeh
Hoto: picture alliance/AP Photo/J. Delay

A ranar daya ga watan Disambar bara ne dai al'ummar kasar ta Gambiya suka fita kada kuri'a a zaben da ya zama zakaran gwaji na gwada karfin ‘yan adawa a kasar, ya kuma zama zaben da sakamakonsa ya ba wa Shugaba Yahya Jammeh shan kayi, wani abu da ake ganin ya bude babi na sabuwar gwamnati a kasar bayan shekaru 22 da Shugaba Jammeh ya yi ya na mulki a wannan kasa .

 Da fari dai Shugaban ya nuna alama ta amincewa da shan ka yi abin ya zamo abin mamaki musamman ga kasashen Yammacin duniya da ke masa kallon dan kama karya, sai dai ba aje ko'ina ba shugaban ya yi kwana da kalamansa inda ya ce bai yadda da sakamakon ba, dan haka ya nemi a sake komawa akwatin kada kuri'a , baya ga bayyana shirinsa na kalubalantar sakamakon zaben a kotu.

Gambia nach Präsidentschaftswahl - Wahlsieger Adama Barrow
Hoto: Getty Images/AFP/Sellou

A lokacin takarar zaben dai na Gambiya  Barrow ya yi alkawari na sake mayar da kasar cikin kungiyar kasashe masu magana da harshen Ingilishi ta Kwamanwel da mutunta tsare-tsare na kotun kasa da kasa mai hukunta masu manyan laifuka  ICC ya kuma yi alkawari na samar da sauyi a tsarin tsaron kasar ta Gambiya  in da ya ce zai kokari ya ga sun nesanta da harkokin siyasa.

Rayuwar cikin gida

A harkokin da suka shafi gida kuwa Barrow na da mata ne guda biyu da yara biyar, ya kuma kasance Musulmi mai  bin tafarkin Sunnah, ya na kuma son kulob din Arsenal idan ana magana ta fuskar wasanni.

Nasaba ta kabila

Ya fito daga kabilar Fula wacce jam'iyyar UDP ke cewa su ne na biyu mafiya  girma cikin kabilun Gambiya , wasu rahotanni n kuma na cewa dan Mandika ne kabila ta farko kuma ita ce kabilar mahaifinsa, mahaifiyarsa Fula. Ya dai girma ya na magana da harshen Fula  kuma matansa biyu ma duk 'yan kabilar ta Fula ne.