A Tunisiya an harbe wani dan adawa
July 25, 2013Talla
Wani labari da ya fito daga kasar Tunisiya na cewa an harbe wani ƙosa a jam'iyar adawan ƙasar kasar. Labarin wanda wani gidan radio a yankin da aka yi harbin ya fara fitarwa, yace an harbe Mohamed Brahmi har lahira a Tunis babban birnin ƙasar Tunisiya. Watanni shida da suka gabata ne dai, aka harbe wani fitaccen dan adawa Chokri Belaid, abinda ya yi sanadiyar barkewar zanga-zanga a fadin ƙasar. Kasar Tunisiya dai har yanzu ba ta samu kammala inganta matakan tsaro ba, tun bayan juyin juya hali, wanda ya kifar da gwamnatin a bisa boren talakawa.
Mawallaf: Usman Shehu Usman
Edita: Mohammed Nasir Awal