A ƙasar Masar tarzuma na ƙara bazuwa
October 8, 2013Wani da ake zargi mai taɗa ƙayar baya ne ya hallaka mutane aƙalla tara a birnin Isma'iliyan ƙasar Masar, kwana guda bayan arangamar jami'an tsaro da masu adawa da juyin mulki ta yi sanadiyar mutuwar mutane dadama. Kazalika wani bam da aka ɗana cikin mota ya hallaka mutane uku kana ya jikkata wasu dadama a yakin Sinai. Fatan kawo ƙarshen tarzuma ya bi ruwa bayan da aƙalla aka hallka ma goya bayan Muhammed Mursi 50, biyo arangamar jami'an tsaro da masu adawa da juyin mulki. Tun bayan kifar da gwamnati Mohammed Mursi magoya bayansa suke tada ƙayar baya. Rikicn baya-bayannan dai ya ɓarke ne a lokacin da 'yan sanda suka yi amfani da ƙarfi don kawar da sansanoni biyu da magoya bayan Mursi suka kafa, a lokacin bikin cika shekaru 40 bayan yaƙin Isra'ila da ƙasashen Larabawa.
Mawallafi: Usman Shehu Usman
Edita: Umaru Aliyu