1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙungiyar 'yan tawayen M23 na Kwango na cikin halin tsaka mai wuya

March 2, 2013

Dakarun gwamnati a Kwango sun ƙwace iko da garin Rutshuru da ke a yankin gabanshin ƙasar, arewa da Goma,ba tare da shan wani gumurzu ba.

https://p.dw.com/p/17pKB
M23 rebels withdraw from the Masisi and Sake areas in the eastern Congo town of Sake, some 27 kms west of Goma, Friday Nov. 30, 2012. Rebels in Congo believed to be backed by Rwanda postponed their departure Friday from the key eastern city of Goma by 48 hours for “logistical reasons,” defying for a second time an ultimatum set by neighboring African countries and backed by Western diplomats. The delay raises the possibility that the M23 rebels don’t intend to leave the city they seized last week, giving credence to a United Nations Group of Experts report which argues that neighboring Rwanda is using the rebels as a proxy to annex territory in mineral-rich eastern Congo.(Foto:Jerome Delay/AP/dapd).
Hoto: AP

Sojojin gwamnatin sun yi amfani da saɓanin da ke tsakanin dakarun ƙungiyar ta M23 domin karɓe iko da garin, wanda 'yan tawayen ke riƙe da shi tun a cikin watan Yulin da ya gabata.

Masu aiko da rahotannin sun ce mazauna garin sun yi tarbo mai daraja ga sojojin gwamnatin,waɗanda suka shiga birnin da 'yan tawayen da ke cikinsa suka tsere suka bar shi, saboda faɗan da ɓangarorin biyu suke kabsawa.Tsakanin magoya bayan janar Sultanin Makenka da Jean Marie Runiga masu yin rikici kan shugabancin ƙungiyar ta M23.tun lokacin da a ka rataɓa hannu a kan wata yarjejeniyar zaman lafiya a ƙasar Habasha tsakanin ƙasashen da ke maƙoftaka da Kwangon domin sake dawo da zaman lafiya a ƙasar.

Mawallafi: Abdourahamane Hassane
Edita : Mohammad Nasiru Awal