1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙungiyar ASUU ta janye yajin aiki

December 17, 2013

A Tarrayar Najeriya ƙungiyar malaman jami'a ta ASUU ta kawo ƙarshen yajin aikin da ta kwashe kusan watannin shida tana yi.

https://p.dw.com/p/1Ab6U
Protestierende Studenten während ASUU Streik in Kano
Hoto: DW/N. S. Zango

Jami'an ƙungiyar sun ce sun ɗage yajin aiki ne bayan yarjejeniyar da suka cimma tsakaninsu da gwamnatin, wacce ta zuba wasu tsabar kuɗaɗe domin tafiyar da harkokin jami'o'i a Najeriya.

A cikin watan Yuli da ya gabata ne ƙungiyar malaman jami'ar ta shiga yin yajin aikin,saboda zargin da ta yi wa gwamntin na gaza aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma a shekarun 2009.Wacce ta tanadi ƙara kuɗaɗen albashin na malaman da kuma samar da kayayyakin aiki ga jami'o'in Najeriyar.

Mawallafi: Abdourahamane Hassane
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe