Ƙaruwar ayyukan Alƙa'ida a Yamen
September 24, 2013Talla
A yammacin wannan Talata ne dai ƙungiyar ta Alƙa'ida, ta sako wasu 'yan sanda 21 da ta kame, a wani mummunan farmakin da ta kai makon jiya. Wata majiya ta ce a yankin da ƙabilu suke iko da shi kan tsaunuka aka sako 'yan sandan, waɗanda aka kama a wani sansaninsu da ke yankin. An dai kama 'yan sandan ne bayan wani kwatan ɓauna da aka yi musu a ranar Juma'an da ta gabata. Ƙungiyar Aka'ida dai na da matukar ƙarfi a ƙasar Yamen, musamman a yankunan gabashi da kudanci, inda babu wata hukuma mai ƙarfi da iko a wajen. Ƙasar Yamen a yanzu haka ita ce inda ƙungiyar Alƙa'ida ke horar da mayaƙa, waɗanda ke aikata munanan ayyuka a yakin ƙasashen Larabawa da ma wasu ƙasashen Afirka.
Mawallafi: Usman Shehu Usman
Edita: Saleh Umar Saleh