1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sa-In-Sa tsakanin gwamnati da kungiyoyin Nijar

March 29, 2018

Dangantaka na ci gaba da tsami tsakanin mahukunta da kungiyoyin fararen hula a Jamhuriyar Nijar, bayan turjiya da nuna kyama da masu fafutikar ke yi da tsarin kasafin kudin kasar na bana.

https://p.dw.com/p/2vC8H
Niger Niamey Opposition
Jagororin kungiyoyi a Jamhuriyar NijarHoto: DW/M. Kanta

A Jamhuriyar Nijar alaka na ci gaba da tsami tsakanin mahukunta da kungiyoyin fararen hula a jamhuriyar Nijar, bayan turjiya da nuna kyama da masu fafutikar ke yi da tsarin kasasfin kudin kasar na bana.

Masu gwagwarmayar a wani yankurin, sun yi zanga-zangar da ta kai ga kame jagorinsu bayan haramta harkokinsu da hukumomi suka yi. Hakan ya kuma tayar da wata sabuwar takaddama a kasar, inda ake ci gaba da tsare shugabannin kungiyoyin a ofishin jami'an 'yan sanda cikin kwanakin da suka gabata.

Baya ma ga tsare wasunsu da 'yan sanda suka yi, an ma kaiga gabatar da su gaban kuliya bayan tsanantar turjiyar a fadin kasar.