Ziyara Koffi Annan a Jamhuriyar Demokraɗiyar Kongo
March 21, 2006A rangadin da ya fara nahiyar Afrika, tun ranar 13 ga watan da mu ke ciki, yau ne,Sakatare jannar na Majalisar Ɗinkin Dunia Koffi Annan, ya kai ziyara kwanaki 3, a Jamhuriya Demokraɗiyar Kongo.
Bayan ƙasashen Afrika ta kudu, Madagaskar, da Kongo-Brazaville, Annan ya sauka yau,a birnin Kinshassa, inda zai tantana da shugaban ƙasa Lauran Kabila, da mataimakan sa 4, da kuma shugaban tawagar Majalisar Ɗinki Dunia, William Swing .
Mahimman batutuwa da za su maida hankulla a kai, sun haɗa da, bitar halin da ake ciki ,ta fannin zaman lahia, da kuma shirye shiryen zaɓen shugaban ƙasa da za ayi, a watan juni na wanna shekara.
A gobe idan Allah ya kai mu, Anan zai kiri taron manema labarai, a birnin Kinshassa, kamin ya tashi zuwa Kisangani da ke arewa maso gabacin ƙasar, yankin Majalisar Ɗinkin Dunia, ta tare dakarun ta.
A wannan yanki da ke fama da tashe tashen hankulla, Majalisar, na da dakaru fiye da18.000 , wanda ke tallafawa gwamnatin riƙwan ƙwarya, a ayyukan ta, na samar da zaman lahia.
Majalisar Ɗinkin Dunia, ta buƙaci ƙungiar gamaya turai, ta aika dakaru, domin ƙara ƙarfi ga tawagar ta.
Babban yaunin da ya rataya a kan wannan rudunoni soja, shine tabbattar da, an shirya zaɓen na watan yuni cikin lumana.