1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jami'an tsaro na azabtar da 'yan adawa

Zainab Mohammed Abubakar
August 4, 2020

Shugaban Zimbabuwe ya ayyana babbar jam'iyyar adawar kasar a matsayin ta ta'addanci, tare da lasar takobin cigaba da kamen 'yan adawa da masu sukar manufofin gwamnati.

https://p.dw.com/p/3gP5S
Simbabwe Wahl | Emmerson Mnangagwa, Präsident
Hoto: picture-alliance/Photoshot/S. Jusa

A jawabinsa ta gidan talabijin na kasar a wannan Talatar, shugaba Emmerson Mnangagwa ya bayyana masu sukarsa a matsayin fitinannu da basa son zaman lafiya, wadanda ya zamanto wajibi a dauki mataki a kansu.

Tun a makon da ya gabata ne dai aka fara kamen, bayan da jami'an soji da na 'yan sandan Zimbabuwen suka tarwatsa gangamin adawa da Mnangagwa. Gwamnatin dai na zargin hadin baki da makiyan kasar daga ketare.

Jawabin na Mnangagwa na zuwa ne adaidai lokacin da gwamnatinsa ke fuskantar suka na cikin gida da ketare dangane da karuwar batutuwan take hakkin bil adama.