1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zimbabuwe ta kaddadamar da shirin yaki da cin hanci

Zulaiha Abubakar
December 15, 2019

Hukumar yaki da cin hanci ta kasar Zimbabuwe ta kame matar mataimakin shugaban kasar Mary Mubaiwa, sakamakon samun ta da laifin cin hanci da musayar kudaden da yawansu ya kai dala miliyan guda ba bisa ka'ida ba.

https://p.dw.com/p/3Urfc
Simbabwe Zusammenstöße mit der Polizei wegen Demonstrationsverbot in Harare
Hoto: Reuters/P. Bulawayo

Hukumar yaki da cin hanci na cigaba da aikin bankado jami'an gwamnatin Zimbabuwe da suka azurta kan su da kudin kasar, cikin wani aikin farfado da tattalin arzikin kasar da shugaban kasar ya kaddamar.

Tun da farko hukumar ta gano yadda matar mataimakin shugaban kasar ta mallaki wani katafaren gida a rukunin gidajen masu hannu da shuni a kasar Afrika ta Kudu. Har yanzu mataimakin shugaban kasar Constantino Chiwenga wanda ya jagoranci hambarar da gwamnatin shugaba Robert Mugabe ya tsuke bakinsa game da tuhumar da matar ta sa ke fuskanta. Kasar Zimbabuwe dai ta kara tsunduma matsalar tattalin arziki jim kadan bayan darewar shugaba Emmerson Mnangagwa karagar mulki duk kuwa da irin alkawurran da ya daukar wa al'ummar na inganta al'amura cikin kankanin lokaci.