1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zargin tilasta yin karya kan kisa a Ruwanda

Yusuf Bala Nayaya
November 2, 2017

Kungiyar kare hakkin bil Adama ta Human Rights Watch ta zargi jami'an gwamnati da na tsaro a Ruwanda da laifin daure wasu iyalai saboda kin bada labaran karya kan dalilan mutuwar 'yan uwansu.

https://p.dw.com/p/2msdk
Ruanda vor den Wahlen 2017
Hoto: Imago/Zumapress/M. Brochstein

A cewar kungiyar jami'ai a Ruwanda na yin barazana ga iyalai don tilastasu su ce ba jami'an tsaron gwamnati ba ne suka kashe musu 'yan uwansu.

Hukumar kare hakkin jama'a a kasar ta Rwanda ta kalubalanci rahoton na Human Rights Watch inda ta ce wasu da ake cewa sun mutu a rahoton da kungiyar ta fitar suna nan a raye, kuma ma da yawa rashin lafiya suka yi suka rasu a cewar shugabar hukumar ta Rwanda Nirere Madeleine.

Kasar ta Ruwanda dai ta saba karyata rahotanni na kungiyoyin kare hakkin bil Adama ciki kuwa har da batun yadda jami'an tsaro ke gallazawa mutanen da ke tsare a hannunsu.