1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zangar adawa da mulki Kabila

Ahmed Salisu MNA
February 24, 2018

Masu adawa da cigaba da zaman Joseph Kabila na Jamhuriyar Demokradiyar Kwango a kujerar shugaban kasa da ke samun goyon bayan cocin Katolika na kasar za su yi zanga-zanga a gobe don matsa masa kan ya sauka daga mulki.

https://p.dw.com/p/2tGWI
Joseph Kabila Präsident der Demokratischen Republik Kongo
Hoto: picture-alliance/dpa/M. Kappeler

Kungiyar nan ta Lay Coordination Comittee (CLC) ce ta kira wannan zanga-zanga ta ranar Lahadi inda al'ummar kasar za su bazama kan tituna neman Kabila ya bar mulki. Gabannin fara wannan zanga-zanga, mabiya darikar Katolika da dama kasar sun gudanar da addu'o'i na musamman a jiya Juma'a, inda wasu daga cikin limaman cocin Katolikar kasa suka bukaci mabiya addinin Kirista da su shiga a dama da su a zanga-zangar wadda suka ce ta lumana ce.