Matsalar rashin tsaro a Jihar Zamfara ta yi kamari
September 1, 2021Talla
Daukar matakin ya biyo bayan satar wasu daliban sama da guda dari a makarantar sakandiren Kaya da ke karamar hukumar Muradun da ke cikin jihar ta Zamfara da wasu yan bindigar suka yi. Wakilin DW a Katsina ya ce satar daliban na zuwa ne bayan da gwamnatin Jihar ta zamfara ta dauki matakan rufe kasuwannin jihar da hana yawo da babura mutum uku.