Zaben Tunisiya na gudana lafiya
October 26, 2014Talla
Masu aiko da rahotanni sun ce mutane da dama na kan dogayen layuka inda suke shirin kada kuri'a a sassa daban na Tunis babban birnin kasar.
Firaministan kasar Mehdi Jomaa ya ce zaben na yau abu ne na tarihi inda a hannu guda ya jinjinawa al'ummar kasar dangane da yadda suka yi fitar dango wajen zaben mutanen da za su wakilce su.
Ya zuwa yanzu dai ba a samu labarin tashin hankali ba ko da dai dama mahukuntan kasar sun ce sun tsaurara matakan tsaro a wuraren zabe wanda takara ta fi zafi tsakanin jam'iyyar Ennahada ta Rachid Ghannouchi da kuma Nidaa Tounes da Beji Caid Essebsi ke jagoranta.