1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaben kasar Chadi

May 2, 2006
https://p.dw.com/p/Buzr

A gobe ne idan Allah ya kai mu, alúmar kasar Chadi za su fita domin kada kuriá a zaben da ake sa ran shugaban kasar Idris Deby zai sake yin tazarce a karo na uku na wasu shekaru biyar a karagar mulki. Sai dai a hannu guda jamaá da dama ba su dauki zaben da wani karsashi ko muhimmanci ba. A bangare guda kuma

hukumar kula da yan gudun hijira ta majalisar dinkin duniya ta baiyana damuwa a game da karuwar hare hare a kusa da sansanonin yan gudun hijira a gabashin Chadi kwana guda bayan da wasu yan bindiga dadi su kimanin 150 suka kashi mutane hudu a wani kauye dake kusa da sansanin yan gudun hijirar. Yan tarzomar wadanda mazauna yankin suka baiyana da cewa ya bangar Janjaweed ne sun yiwa kauyen kawanya inda suka bude wuta a kan mai uwa da wabi.