1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An zargi al-Bashir da laifin cin hanci da rashawa

Ramatu Garba Baba
June 13, 2019

Masu shigar da kara sun ce bincike da aka gudanar ya sami tsohon Shugaban kasar Oumar Hassane al-Bashir da hannu a laifukan cin hanci da rashawa da ke bukatar a soma tuhumarsa.

https://p.dw.com/p/3KO5G
Sudan April 2019 | Omar al-Baschir, Präsident
Hoto: Reuters/M. Nureldin Abdallah

Wata sanarwa da masu shigar da kara suka fitar a wannan Alhamis ce ta tabbatar da hakan, inda a ciki aka nemi a soma tuhumar shugaban da matsin masu zanga-zanga ya kawo karshen mulkinsa na shekaru talatin. Sakamakon binciken dai, wanda aka soma gudanarwa ne tun bayan da aka hambarar da gwamnatinsa a watan Febrairun da ya gabata. 

An dade ana neman a mika al-Bashir gaban kotun kasa da kasa ta ICC wacce da ma ta ba da sammacin kamo shi tun a shekara ta 2009 a bisa zargin aikata kisan kiyashi a yakin Darfur da kuma na baya-bayan nan, gano tarin daloli da aka yi a muhallinsa bayan da aka kai shi gidan yari a karshen mulkinsa.

Tsugune dai ba ta kare ba a Sudan kan rikicin samar da gwamnati, a yau ne aka soma wani zagayen ganawa a tsakanin jagoran mulkin soji na riko da wasu wakilai na Amirka da Afirka inda ake sa ran za su lalubo hanyar kawo karshen rikicin dama samar da sabuwar gwamnati.