1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yunkurin kasashen Turai na magance kin biyan haraji

April 13, 2013

Kasashen Tarayyar Turai ashirin da bakwai za su kafa wani kwamiti da zai yi yaki da masu kin biyan haraji.

https://p.dw.com/p/18FPT
Flags of the European Union countries are hoisted in front of the European Parliament on August 1, 2010 in the French eastern city of Strasbourg. AFP PHOTO / JOHANNA LEGUERRE (Photo credit should read JOHANNA LEGUERRE/AFP/Getty Images)
Friedensnobelpreis EU Europäische Union SymbolbildHoto: Getty Images/AFP

Shugaban hukumar tarayyyar Turai Herman van Rompuy ne ya shaida hakan a jiya Juma'a inda ya kara da cewar kasashen za su dauki wannan mataki ne a taron da za su yi cikin watan Mayu mai zuwa domin kuwa masu kin biyan haraji na jawowa nahiyar asarar kudin da yawasa ya kai yuro zambar miliyan guda a kowacce shekara.

Van Rumpoy ya ce taron zai yi amfani da wannan dama ce domin kawar da duk wata kariya ta siyasa da masu kin biyan haraji ke amfani da ita wajen aikata wannan laifi to sai dai kasashen irin su Austriya na kokarin turewa wannan yunkuri.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Muhammad Awal Balarabe