1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yemen: Annobar cutar kwalara ta yi kamari

Salissou Boukari
July 23, 2017

Sakamakon matsalolin kiwon lafiya da ake fuskanta a kasar Yemen, kungiyar bada agaji ta kasa da kasa ta Red Cross CICR ta yi hannunka mai sanda kan yadda annobar cutar kwalara ke dada kamari.

https://p.dw.com/p/2h1uA
Jemen Cholera
Hoto: Picture alliance/Photoshot/M. Mohammed

Kawo yanzu dai cutar ta kwalara ta yi sanadiyyar mutuwar mutane dubu daya da 800 a cewar Kungiyar ta CICR wadda kuma ta ce idan ba a yi hattara ba adadin wadanda za su kamu da cutar a wannan shekara ta 2017 zai kai na mutane dubu 600. Bincike ya nunar cewa cikin mutane 45 na kasar mutun daya na dauke da cutar ta kwalara a cewar kungiyar agajin cikin wata sanarwa da ta fitar, inda ta ce hakan kuma ba komai ba ne illa sakamakon yake-yaken da ya lalata muhimman gine-ginen kasar tare da durkusar da tsarin kiwon lafiya baki daya.