1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yarjejeniya tsakanin Iran da IAEA

November 11, 2013

Kasar Iran ta amince jami'an hukumar makamashin nukiliya ta duniya IAEA sun bincika tashoshinta da ake ganin za ta iya amfani da su wajen kera makamin kare dangi.

https://p.dw.com/p/1AFLu
Head of Iran's Atomic Energy Organisation Ali Akbar Salehi (L) shakes hands with International Atomic Energy Agency (IAEA) Director General Yukiya Amano, during their meeting in Tehran on November 11, 2013. Amano arrived in the Iranian capital to discuss Iran's nuclear programme after top world diplomats fail to clinch a long-sought deal to curb Tehran's nuclear activities but insist they are narrowing the gaps. AFP PHOTO/ATTA KENARE (Photo credit should read ATTA KENARE/AFP/Getty Images)
Hoto: Getty Images/Afp/Atta Kenare

Hukumar makamashin nukiliya ta duniya ta cimma yarjejeniya da Iran a kan shirinta na inganta wannan makamashi da ake takaddama akai. Babban jami'in da ke kula da harkokin nukiliya na Iran Ali Akbar Salehi ne ya yi wannan sanarwa a birnin Teheran, bayan da ya rattaba hannu akan yarjejeniya da shugaban IAEA Yukiya Amano.

Sassa biyu sun amince jami'an IAEA sun rika bincika daukacin cibiyoyin nukiliyar da Iran ta mallaka, ciki kuwa har da na Parchin da ke cikin yankin kudu masu gabashin kasar. Hukumomin leken asiri na kasashen Turai suna zargin Iran ta neman amfani da wannan tashar wajen kera makamin kare dangi.

Da farko dai Iran da sauran kasashen nan biyar da ke da kujarar din-din-din a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da kuma Jamus sun watse a taronsu ba tare da cimma matsaya ba a birnin Jeniva.

Sai dai kuma wannan birni zai dauki bakwancin wani sabon zaman tattaunawa tsakanin manyan kasashen duniya da kuma Iran a ranar 20 ga wannan wata na Nowamba idan Allah ya kaimu.

Mawallafi: Mouhamadou Awal Balarabe
Edita: Umaru Aliyu