1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan PDP sun yi zanga-zanga a Sokoto

Ahmed Salisu
March 12, 2019

'Yan jam'iyyar PDP a jihar Sokoto da ke arewacin Najeriya sun gudanar da zanga-zanga a bakin ofishin hukumar zaben jihar inda suka bukaci da a bayyana sakamakon zaben gwamna.

https://p.dw.com/p/3ErLg
Nigeria Regierungspartei PDP
Hoto: DW/K. Gänsler

Zanga-zangar ta biyo bayan sanarwar da hukumar zaben kasar ta yi cewar zaben jihar bai kammala kasancewar an soke zabuka a mazabu 139 na jihar saboda dalilai daban-daban.

Takara a zaben na Sokoto dai ta fi zafi tsakanin Aminu Waziri Tambuwal na jam'iyyar PDP da ke neman wa'adi na biyu da kuma Ahmed Aliyu na jam'iyyar APC mai mulkin kasar.