1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hare-haren 'yan jihadi na kara yawaita a Mali

Salissou Boukari
July 16, 2018

Wasu mutane da ake kyautata zaton mayakan jihadi ne sun kai hari tare da hallaka gwamman fararan hulla a yankin Arewa maso gabashin kasar Mali a cewar hukumomin kasar.

https://p.dw.com/p/31VbM
Islamisten Bewegung Jihad in West Afrika
Hoto: Getty Images

A 'yan watannin baya-bayan nan dai daruruwan fararan hulla ne da suka hada da Fulani da Abzinawa 'yan jihadi suka hallaka. Ko a yammcin ranar Lahadi ma dai wasu 'yan bindiga da suka saba gudanar da muyagun ayyukansu kusa da iyakar kasar ta Mali da Jamhuriyar Nijar, sun kai hari a garin Injagalane da ke yammacin birnin Menaka, kaman yadda wata sanarwa ta hadin gwiwa ta mayakan kungiyoyi biyu na Abzinawa da ke marawa sojojin kasar Faransa baya ta bayyana.

Mutanen dai dauke da makammai sun zo ne bisa babura lokacin da suka shiga garin na Injagalane kuma suka yi harbin kan mai uwa da wabi cikin jama'a inda suka kashe mutane 14 tare da kona motoci da babura da dama acewar hukumomin jihar ta Menaka.