1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan al-Shabaab sun sake kwace wasu wurare

Salissou BoukariJuly 3, 2015

Dakarun Tarayyar Afirka a Somaliya na Amisom sun janye daga wasu mahimman wuraren kasar sakamakon yawaitar hare-haren 'yan kungiyar al-Shabbab.

https://p.dw.com/p/1FsMG
Al-Shabaab Kämpfer in Somalia
Hoto: Getty Images/AFP/M. Abdiwahab

A cewar hukumomin kasar, janyewar dakarun na Tarayyar Afirka ya shafi yankuna Qoryoley da Awdhegele wadanda suka sake fadawa a hannayen 'yan kungiyar ta al-Shabaab.

A cewar mazauna wannan yanki, tuni dai 'yan kungiyar ta al-Shabbab suka kafa tutarsu a garuruwan da suka kwace, kuma babu sojan kiyaye zaman lafiya ko daya a yankin da ke a nisan km akalla 80 da Mogadiscio babban birnin kasar.

Daga nashi bangare Shugaban gundumar ta Awdegele Mohamed Aweys ya tabbatar cewa shi ma ya fice daga wannan birni.