Wakilan Afirka a Doha sun samu lambobin zinare
October 7, 2019Talla
'Yan wasan guje-guje da tsalle-tsalle na kasashen Afirka ta yi musu kyaun rufi a ranar karshe ta gasar duniya da ke gudana a birnin Doha na kasar Qatar, inda akasarinsu wadanda suka zage dantse sun tashi da lambobin zinare. Kwanaki goma aka shafe ana fafatawa a wasanni 49 na maza da na mata kama daga na harbin mashi zuwa ga tsalle-tsalle tsakanin 'yan wasa kimanin 2000 na kasashe 209 na duniya.Za ku iya samun karin bayani a cikin sautin da ke dauke da labarin wasanni a kasa.