1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan adawa a Burundi sun dauki sabon salo

Yusuf BalaJune 9, 2015

A cewar mai magana da yawun gwamnatin kasar ta Burundi Willy Nyamitwe, yadda 'yan adawar suka yi kunnen uwar shegu da bukatar Majalisar alama ce ta rashin mutuntawa.

https://p.dw.com/p/1Fe4J
Burundi Oppositioneller festgenommen
Hoto: picture-alliance/AP Photo/Delay

Kungiyoyin fafutika a kasar Burundi a ranar Talatan nan sun yi fatali da bukatar mai shiga tsakaninsu da bangaren gwamnati daga Majalisar Dinkin Duniya, inda suka bayyana shi da cewa take-takensa sun nuna alamun goyon bayan shugaba Pierre Nkurunziza mai muradin yin tazarce a karo na uku.

Kungiyoyi masu fafutika da dama sun tura wasika zuwa babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon, inda cikin wasikar suka ce mai shiga tsakanin daga kasar Aljeriya Said Djinnit, suna da tantama kan aikinsa a cewar Pierre Claver Mbonimpa, da ke gaba-gaba cikin masu adawa da tazarcen na shugaba Nkrunziza.

A cewar mai magana da yawun gwamnatin kasar ta Burundi Willy Nyamitwe, yadda 'yan adawar suka ki mutunta bukatar ta jami'in diplomasiya Djinnit, alama ce ta rashin nuna dattako