1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan Ƙungiyar Boko Haram sun ƙwace garin Michika

September 7, 2014

Rahotanni daga Jihar Adamawa da ke yankin arewa maso gabashin Najeriya na cewar 'yan Ƙungiyan Boko Haram sun karɓe iko da ƙaramar hukumar Michika.

https://p.dw.com/p/1D8OK
Boko-Haram-Chef Abubakar Shekau BITTE BESCHREIBUNG BEACHTEN / SCHLECHTE QUALITÄT
Hoto: picture-alliance/dpa

Shaidu mazauna garin na Michika sun shida wa DW cewar 'yan ƙungiyar sun kafa tuttarsu suna kuma ta yin sintiri a cikin garin, yayin da jama'ar garin suka kiɗime suna ƙoƙarin ƙaurace wa birnin.

Kuma a halin da ake ciki al'ummar ƙaramar hukumar Mubi na cikin zaman ɗar-ɗar da kuma fargabar abin da ka iya biyo baya inda tuni wasu suka soma ficewa daga yankin.

Mawallafi : Abdulraheem Hasan / Abdourahamane Hassane
Edita : Mohammad Nasiru Awal