'Yan Ƙungiyar Boko Haram sun ƙwace garin Michika
September 7, 2014Talla
Shaidu mazauna garin na Michika sun shida wa DW cewar 'yan ƙungiyar sun kafa tuttarsu suna kuma ta yin sintiri a cikin garin, yayin da jama'ar garin suka kiɗime suna ƙoƙarin ƙaurace wa birnin.
Kuma a halin da ake ciki al'ummar ƙaramar hukumar Mubi na cikin zaman ɗar-ɗar da kuma fargabar abin da ka iya biyo baya inda tuni wasu suka soma ficewa daga yankin.
Mawallafi : Abdulraheem Hasan / Abdourahamane Hassane
Edita : Mohammad Nasiru Awal