1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan ƙasar Zimbabwe sun fito don jefa ƙuri'a

Usman ShehuJuly 31, 2013

An sanar da cewa jama'a na can na gudanar da zaɓen a ƙasar Zimbabwe, inda kawo yanzu komai ke gudana ba tare da tashin hankali ba

https://p.dw.com/p/19HYH
Zimbabweans queue to cast their ballots in the country's general elections in Harare, July 31, 2013. Zimbabweans began voting in a fiercely contested election pitting President Robert Mugabe against Prime Minister Morgan Tsvangirai, who has vowed to push Africa's oldest leader into retirement after 33 years in power. REUTERS/Philimon Bulawayo (ZIMBABWE - Tags: POLITICS ELECTIONS)
Masu kada uri'a a Zimbabwe cikin dogon layiHoto: Reuters

A ƙasar Zimbabwe an buɗe rumfunan zaɓe, don zaɓar sabon shugaban ƙasa da 'yan majalisun dokoki. Daga cikin 'yan takara biyar, waɗanda suka fi fice sune Morgan Tsvangirai ɗan shekaru 61 a duniya na jami'iyyar MDC, sai kuma shugaba Robert Mugabe ɗan shekaru 89 da haifuwa na ZANU-PF, wanda ke mulkin ƙasar tun bayan samun yancin kai a shekara ta 1980. Wani ɗan takarar da zai yi tasiri a zaben na Zimbabwe shine Dumiso Dabengwa. Ya kasance tsohon ministan harkokin cikin gida a gwamnatin Mugabe, amma yanzu shi ne shugaban jam'iyyar ZAPU da ya sake farfaɗowa. Jam'iyyar dai ta sake samun 'yan zaman kanta bayan da ta balle daga haɗakar ta tilas da jam'iyyar Mugabe ta ZANU-PF a shekara ta 1989. A shekara ta 2008 dai Dabengwa ya goyi bayan 'yan adawa, amma a yanzu shi kansa zai ƙalubalanci Mugabe a wannan zaɓen.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Uamru Aliyu