1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yammacin Afrika tayi a dabo da cutar Ebola

Kamaluddeen SaniJanuary 14, 2016

A ranar Alhamis din nan ce hukumar lafiya ta duniya WHO ta bayyana cewar an sami nasar kakkabe kwayar cutar Ebola daga kasashen yammacin nahiyar Afrka baki daya.

https://p.dw.com/p/1HdgJ
Symbolbild - Ebola
Hoto: Getty Images/J. Pollex

Kwararru da ke cikin hukumar ta WHO, sun kuma yi gargadi cewar duk da nasarar da aka samu, to kuwa a hannu daya dole ne a cigaba da taka tsan –tsan don kaucewa sake bullar cutar ta Ebola.

Bayanin kakkabe kwayar cutar ta Ebola a yammacin Afrika ya shafe kwanaki 42 bayan tabbatar da bullar kwayar cutar ta karshe a kasar Laberiya, dake kasancewa kasa ta karshe a yammacin Afrika da cutar ta fi kamari.

Fiye da mutane sama da dubu goma sha daya ne suka mutu sakamakon bullar kwayar cutar ta Ebola a shekara ta 2013, a yayin da karin wasu sama da dubu 28 suka kamu da kwayar cutar.