1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yaki da cin hanci da rashawa a Iraki

Ahmed SalisuDecember 8, 2014

Firaminsitan Iraki Haider al-Abadi ya ce barazanar da kasarsa ke fuskanta ta cin hanci da rashawa ba ta da banbanci da ta 'yan ta'adda wanda suke hallaka mutane.

https://p.dw.com/p/1E183
Irak Ministerpräsident Haider al-Abadi in Bagdad
Hoto: Reuters

Al-Abadi ya ce gwamnatinsa a tsaye ta ke don yakar cin hanci ko da kuwa hakan ne zai sanadin rayuwarsa inda ya kara da cewar tuni ma suka fara bankado wasu shafaffu da mai kuma za su yi kokarin ganin sun fuskanci hukunci.

A karshen watan da ya gabata ne dai firaministan na Iraki ya ce wani bincike da aka gudanar ya gano cewar akwai ma'aikatan bogi dubu 50 da ya gada a rundunar sojin kasar wanda ake fidda albashi da sunansu.

To sai dai wanda ya gada din Nuri al-Maliki a wata hira da ya yi da kamfanin dillancin labarai na AFP dazu ya musanta batun ma'aikatan na bogi da mahukuntan Irakin na yanzu suka ce sun gada daga gwamnatin da ya jagoranta.