Wani mutum ya harbe dalibai uku a Amirka
February 14, 2023Talla
Maharin bakar fata ya harbe dalibai uku har lahira tare da jikkata wasu biyar da aka kwantar a gadon asibiti kafin daga bisani ya ranta a na kare.
Sai dai bayan baza dariruwan jami'an 'yan sanda domin farautar maharin tare da yada hutunansa an tsinto gawarsa a kusa da inda ya kai harin shima ya kashe kansa bayan ya yi wannan aika-aika.
Tuni dai aka dakatar da harkoki a jami'ar tare da kiran dalibai kusan dubu 50 da ke karatu a ciki da kuma ma'aikata da su killace kansu.
A shekarun baya-baya nan dai ana dada samun karuwar kisa ta hanyar yin anfani da bindiga a kasar Amirka lamarin da ake alankantawa da bazuwar makamai a kasar inda aka kiyasta cewa magidanta biyu cikin uku a Amirka sun mallaki bindiga.