1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

UNICEF: Rikicin Gabas ta Tsakiya na hallaka yara

Abdul-raheem Hassan
February 5, 2018

Fiye da kananan yara 80 ne aka kashe a yankunan da ke fama da tashe-tashen hankula a Gabas ta Tsakiya, musamman kasar Siriya a cikin watan Janairun da ya gabata.

https://p.dw.com/p/2sAPk
UNICEF Foto des Jahres
Hoto: Zohra Bensemra/Reuters

Asusun kula kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya ya ce watan Janairun 2018, ya kasance bakar wata ga kananan yara ganin yadda aka zubda jinin yara a kasasahen Iraki da Siriya da Falatsinu da Yemen da kuma Libiya.

UNICEF ta ce ba za a bari jinin yaran ya bi ruwa ba, wajibi a su taimaka a daga muroyoyin wadanda ba hali su bayyana kukansu. A don haka suke kira da a kawo karshen afkawa kananan yara a lokutan yaki.  

Wasu alkaluma da MDD ta wallafa ya nuna cewa an kashe kananan yara 59 a Siriya, yayin da kasar Yemen ke biyemata cikin kashen da akafi salwantar da rayuwar yara.