1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fafaraoma Francis zai kai ziyara Daular Larabawa

Ramatu Garba Baba
February 3, 2019

A wannan Lahadin, shugaban darikar katolika na duniya Fafaroma Francis zai ziyarci Hadaddiyar Daular Larabawa inda zai halarci wani taro na sasanta tsakanin mabiya addinai.

https://p.dw.com/p/3CdkE
Vatikanstadt Papst Franziskus Messe im Petersdom
Hoto: Getty Images/AFP/T. Fabi

Rahotannin na nuni da cewa ya karbi goyon gayyata ne daga yerima mai jiran gado na kasar Sheikh Mohammed Bin Zayed al-Nahyan. Gabanin ziyarar, shugaban cocin katolikan ya baiyana damuwa kan yakin kasar Yemen na fiye da shekaru hudu, inda ya shawarci bangarorin da ke rikici da juna da su amince da yarjejeniyar zaman lafiya domin bayar da daman shigar da agaji ga mabukata da rikicin ya kassara.

Francis ya kasance Fafaroma na farko da ke irin wannan ziyara a yankin kasashen Larabawa a tarihi.