1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shirin daukar matakin soji a Siriya

Binta Aliyu Zurmi
May 31, 2022

Turkiyya na shirin daukar matakin soji a kan mayakan kurdawa na YPG da ke arewacin Siriya. Ankara na ganin rashin mutunta yarjejeniyar da aka cimma na yin nesa da iyakarta na barazana ga tsaron kasar.

https://p.dw.com/p/4C4YG
Türkei | Präsident Recep Tayyip Erdogan
Hoto: Turkish Presidency/AP/picture alliance

Shugaba Racep Tayyip Erdogan na Turkiyya ya bayyana shirinsa na yin amfani da karfin soji a yankin arewacin kasar Siriya a yayin da Rasha wacce ke goyon bayan Siriyar ke ci gaba da luguden wuta a Ukraine.

Ankara ta sha alwashin kaddamar da hari a kan mayakan kurdawa na YPG da ke iyakar kasashen biyu.  A wata tattaunawa da Erdogan ya yi da Shugaba Vladmir Putin na Rasha ta wayar tarho, ya bayyana masa cewa yarjejeniyar da suka cimma a shekarar 2019 ta ajiye tazarar a kalla kilomita 30 har yanzu ba ta fara aiki ba. wanda ya ce hakan na barazana ga tsaron kasar.

kasashen Rasha da na Siriya gami da Amirka na da dakarunsu a wannan yanki da ke da iyaka da Turkiyya, sai dai Turkiyya har gobe ta na yi wa mayakan na Kurdawa kallon 'yan ta'adda da ke da alaka da jam'iyya PKK.